Siasia butulu ne, sai mun tona masa asiri-Hukumar NFF
– Kocin Najeriya Samson Siasia ya bayyana cewa ya ajiye aikin horar da Kungiyar U-23 Dream Team ta Kasar.
– Siasia ya jagoranci Dream Team zuwa lashe kyautar na uku a Gasar Rio Olympics.
– Kocin yace Hukumar kwallon kafar Kasar (NFF) ba ta ganin kimar sa.
– Sai dai NFF tace duk laifin Kocin ne da Najeriya ta kasa zuwa Gasar AFCON 2017
– Hukumar NFF ta kasa tace za ta fallasa wanene Siasia.
Hukumar kwallon kafar Kasar Najeriya Watau NFF tace Tsohon Kocin U-23 Dream Team ta Kasar Najeriyar, Siasia butulu ne kuma za ta tona asirin sa.
Wani babban Jami’in Hukumar kwallon Najeriya (NFF) ya bayyana Tsohon Kocin U-23 Dream Team, Samson Siasia a matsayin butulu. Jami’in yace Hukumar za ta cire masa zani a kasuwa idan har bai daina batanci ga Hukumar kwallon kafar Kasar ba.
Kwanan ne dai Kocin ya ci wa Najeriya kyautar tagulla a Gasar 2016 Olympics, ya kuma bayyana cewa shi da Najeriya, ta kare, a a wata hira da yayi. Kocin ya bayyana cewa Hukumar ta NFF ta banzatar da shi kafin wasan da ma lokacin da ake buga Gasar Olympics din.
Kocin ya bayyana yadda aka jibge su a Amurka ana daf da fara Gasar, sai dai suka iso Garin Manuas ana saura kusan awanni biyar a take wasan su da Kasar Japan, wanda suka yi nasara da ci 5-4.
KU KARANTA: BARCELONA TA SAYE GOLA
Sai dai da wani Jami’in Hukumar ta NFF yake maida martani ga Tsohon Kocin ta OwnGoalNigeria.com, yana mai cewa: “Mun gaji da surutan Siasia, mu ma muna da namu ta cewar game da batun… ka da Siasia ya manta cewa dalilin sa ne Najeriya ba za ta samu zuwa Gasar AFCON 2017 ba, duk shi ya ja…” Jami’in ya kara da cewa: “Siaisia ya cika butulu, mun basa wata damar, amma ya kara nuna mana cewa ya cika ba zai taba canzawa, mun san duk abubuwan da yayi lokacin da ya rike Super Eagles, shiru kurum muka yi… Shi ya sani! Ku je ku tambayi korafin da aka kawo mana game da shi. Idan har bai yi mana shiru ba, za muyi maganin sa, sai mun tona masa asiri, mun sa ya kare. Gwal ma ya kamata ace mun ci a Gasar Olympics ba tagulla ba…”
The post Siasia butulu ne, sai mun tona masa asiri-Hukumar NFF appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read Naij.com 24/7.
