Ma’aikacin shugaba Buhari ya rasu
Wani babban ma’aikacin shugaban kasa Muhammadu Buhari akan al’amuran tattalin arziki , Ayodele Adu, ya rasu. Adu ya rasu ranan juma’a,12 ga watan augusta game da labarin da jaridar Naij.com. Babu cikakken bayani akan mutuwan sa a lokacin rubuta wannan labara,amma wata gaisuwan ta’aziya da , Olayinka Oyebode, mai Magana da yawun ministan kayan ma’adinai, […]
The post Ma’aikacin shugaba Buhari ya rasu appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read Naij.com 24/7.
Wani babban ma’aikacin shugaban kasa Muhammadu Buhari akan al’amuran tattalin arziki , Ayodele Adu, ya rasu. Adu ya rasu ranan juma’a,12 ga watan augusta game da labarin da jaridar Naij.com.
Babu cikakken bayani akan mutuwan sa a lokacin rubuta wannan labara,amma wata gaisuwan ta’aziya da , Olayinka Oyebode, mai Magana da yawun ministan kayan ma’adinai, Dr. Kayode Fayemi ya fada , ya saki na tabattar da labarin. Fayemi yayi ta’aziya ga iyalan mutumin tare nuna juyayin sa akan faruwan.
Marigayi Audu yayi aiki a ofishin kamfanin Fountain Investment da ke jihar Ekiti yayinda Fayemi ke gwamnan jihar. Fayemi ya sifanta mutuwan a matsayin babban rashi ne ga jam’iyyar APC da gwamnatin tarayya . Ya ce rasuwan audu ya susa jam’iyyar APC ,shiyar jihar ekiti musamman bayan mutuwan Cif Ibidapo Awojolu da Alhaji Femi Ganiyu Adeyemi.
Ministan ya sifanta kwararren masanin tattalin arzikin a matsayin mutum mai mutunci kuma babban da siyasa,wanda ke shirye da yayi amfani da duka abinda ya mallaka na ilimi domin taimaka ma kasa.
KU KARANTA : INEC ta tantance yan takara 17 na zaben jihar Edo
“Babban dan najeriya ne, dan jihar ekiti mai mutunci wanda yayi gwagwarmaya da kokari har ya kai matsayin da kai akan duka ayyukan da yake yi. Mutum ne mai karfin haling aske, mai hali mai kyau,wanda ke da kishin jihar ekiti. Wannan babban rashi ne . Zamuyi rashin shi.”
Majiya tace Adu wanda yake dan asalin Omuo Ekiti na jihae Ekiti yam utu ne a kasar India bayan doguwar rashin lafiya.
The post Ma’aikacin shugaba Buhari ya rasu appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read Naij.com 24/7.